YANZU-YANZU: Gobara ta tashi a Hedikwatar Ma'aikatar kudi ta Nijeriya dake Abuja.

Gobara ta tashi a hedikwatar ma'aikatar kuɗi ta Najeriya da ke Abuja babban birnin ƙasar.

Babu tabbaci kan ko me ya jawo gobarar sai dai tuni ma'aikatan kashe gobara suka isa wurin.

Jaridar Punch a Najeriya ta ruwaito mai magana da yawun hukumar kashe gobara wato Abraham Paul inda ya ce ma'aikatansu na can suna ƙoƙarin kashe wutar.

A wani saƙo da ma'aikatar kuɗi da kasafi ta Najeriya ta wallafa a shafinta na Twitter, ta ce gobarar ba ta yi muni ba kamar yadda aka yi ta zuzutawa a shafukan sada zumunta inda ta ce wasu batira ne da aka keɓe suka kama da wuta a wani zaure da ke ƙasa a cikin hedikwatar ma'aikatar.



Comments

Popular posts from this blog

Petrol costs N1,826 in Togo, Dangote denies DAPPMAN’s petrol pricing claims

Good day. I'd like to talk about an important topic titled: ‘Nigeria’s Technology Industry: Opportunities in Technology, Media, and Telecommunications.

KASATA NIGERIA: ƘASA MAI ALBARKA, AMMA...?