Zamu yi amfani da karfi wajen hana zanga-zanga - Rundunar ‘yan sanda Osun

 



Rundunar ‘yan sandan jihar Osun ta sha alwashin yin amfani da duk wata hanya da ta dace wajen dakile duk wata zanga-zanga ta kowace hanya, musamman a lokacin zaben gwamnan jihar dake tafe.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Wale Olokode ya ce rundunar ta samu labarin cewa wasu gungun mutane na shirin gudanar da zanga-zanga a jihar.

Da yake gargadin mutane ko gungun mutanen da ke shirin irin wannan a jihar, kwamishinan ‘yan sandan a wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan, SP Yemisi Opalola, ya fitar, ya yi kira ga iyaye da su gargadi ‘ya’yansu da su guji shiga cikin munanan ayyuka a lokacin zabe.

Yayin da yake ba da tabbacin tsaro a lokacin zabukan Olokode ya sha alwashin cewa hukumomin tsaro ba za su yi kasa a gwiwa ba wajen tunkarar duk wani ko wasu mutane da ke yunkurin haifar da matsala tare da kawo cikas ga gudanuwarzabukan cikin tsanaki tare da tabbatar da doka.

Comments

Popular posts from this blog

Petrol costs N1,826 in Togo, Dangote denies DAPPMAN’s petrol pricing claims

Good day. I'd like to talk about an important topic titled: ‘Nigeria’s Technology Industry: Opportunities in Technology, Media, and Telecommunications.

KASATA NIGERIA: ƘASA MAI ALBARKA, AMMA...?